Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da takwaransa na jihar Edo Monday Okpebholo,sun ziyarci garin Torankawa da ke Kano domin jajanta wa al’ummar garin bisa kisan mafarautan nan guda 16 da aka yi a jihar Edo.
Gwamnonin biyu sun ziyarci garin ne da manufar tabbatar wa da iyalan waÉ—anda al’amarin ya shafa cewa lallai gwamnatin jihar Edo za ta hukunta waÉ—anda suka yi wannan aika-aika sannan kuma gwamnatin za ta biya su diyya.
“Wannan ziyara ba kawai ta jaje da ta’aziyya ba ce, a’a ta nuna tabbacin Æ™oÆ™arin samar da adalci. Iyalan waÉ—annan mamata na buÆ™atar abin da ya fi kalaman baka – suna buÆ™atar aiwatar da duk abin da aka faÉ—a za a yi musu. Ba za mu zauna ba har sai mun ga an kama waÉ—anda suka yi wannan aika-aika, sai an yi holinsu a bainar jama’a sannan a hukunta su.” In ji gwamna Abba Kabir.
A nasa É“angaren gwamnan jihar ta Edo, Monday Okpebholo ya miÆ™a ta’aziyyarsa ga iyalan inda ya ba su tabbacin cewa gwamnatinsa za ta yi adalci ba daÉ—ewa ba.