fidelitybank

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Date:

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare da kiran gwamnati ta ɗauki cikin gaggawa domin kawo ƙarshen kashe-kashen.

Tsohon ɗan takarar shuagaban ƙasar na jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, ya nuna damuwa matuka kan ci gaba da zubar da jini a jihar Benue, yana mai kira ga gwamnatin tarayya da ta ɗauki matakin gaggawa domin kawo karshen matsalar tsaro da ke addabar yankin.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X, Atiku ya bayyana halin da ake ciki a matsayin “mummunar masifa” da gwamnatin ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kai.

Atiku ya ce al’ummar Benue na fama da hare-hare na tsawon shekaru, inda rayuka ke salwanta, kauyuka ke lalacewa, iyalai ke rasa muhallansu.

“Buƙatarmu ita ce samun zaman lafiya da noma ba tare da fargabar mutuwa ba, da kuma tarbiyyar ‘ya’yansu cikin kwanciyar hankali.” in ji Atiku.

Ya jaddada cewa wadannan hakkoki ne da ƙundin tsarin mulki na kasa ya tanada, kuma wajibi ne gwamnati ta kare su.

Ya kuma yi Allah-wadai da yadda jami’an tsaro ke amfani da karfi da hayaki mai sa hawaye wajen tarwatsa masu zanga-zangar lumana a Benue da ke neman kariya daga gwamnati.

“Hakan ba salon mulki ba ne, illa zalunci ne da cin amanar shugabanci.” Ya ce hakan yana nuna yadda gwamnati ta yi biris da kukan jama’a.

Atiku ya ƙara da cewa matsalar tsaro ba a Benue kaɗai take ba, har da jihohin Plateau da Zamfara da Kaduna da kuma Taraba, inda jama’a ke fuskantar irin wannan hali.

Ya bukaci shuwagabanni da gwamnatocin jihohi da su mayar da hankali kan kare rayukan ‘yan ƙasa fiye da yin fito na fito da siyasa, ta hanyar aiki da hukumomin tsaro da samar da kayan aiki masu inganci ga yankunan da abin ya shafa.

Hakazalika, Atiku ya yi kira ga ƴan Najeriya da kada su yi shiru a gaban zalunci. Ya bukace su da su ɗaga murya su nemi adalci da aukar mataki.

legits news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp