fidelitybank

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Date:

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare da kiran gwamnati ta ɗauki cikin gaggawa domin kawo ƙarshen kashe-kashen.

Tsohon ɗan takarar shuagaban ƙasar na jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, ya nuna damuwa matuka kan ci gaba da zubar da jini a jihar Benue, yana mai kira ga gwamnatin tarayya da ta ɗauki matakin gaggawa domin kawo karshen matsalar tsaro da ke addabar yankin.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X, Atiku ya bayyana halin da ake ciki a matsayin “mummunar masifa” da gwamnatin ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kai.

Atiku ya ce al’ummar Benue na fama da hare-hare na tsawon shekaru, inda rayuka ke salwanta, kauyuka ke lalacewa, iyalai ke rasa muhallansu.

“Buƙatarmu ita ce samun zaman lafiya da noma ba tare da fargabar mutuwa ba, da kuma tarbiyyar ‘ya’yansu cikin kwanciyar hankali.” in ji Atiku.

Ya jaddada cewa wadannan hakkoki ne da ƙundin tsarin mulki na kasa ya tanada, kuma wajibi ne gwamnati ta kare su.

Ya kuma yi Allah-wadai da yadda jami’an tsaro ke amfani da karfi da hayaki mai sa hawaye wajen tarwatsa masu zanga-zangar lumana a Benue da ke neman kariya daga gwamnati.

“Hakan ba salon mulki ba ne, illa zalunci ne da cin amanar shugabanci.” Ya ce hakan yana nuna yadda gwamnati ta yi biris da kukan jama’a.

Atiku ya ƙara da cewa matsalar tsaro ba a Benue kaɗai take ba, har da jihohin Plateau da Zamfara da Kaduna da kuma Taraba, inda jama’a ke fuskantar irin wannan hali.

Ya bukaci shuwagabanni da gwamnatocin jihohi da su mayar da hankali kan kare rayukan ‘yan ƙasa fiye da yin fito na fito da siyasa, ta hanyar aiki da hukumomin tsaro da samar da kayan aiki masu inganci ga yankunan da abin ya shafa.

Hakazalika, Atiku ya yi kira ga ƴan Najeriya da kada su yi shiru a gaban zalunci. Ya bukace su da su ɗaga murya su nemi adalci da aukar mataki.

the nation news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp