fidelitybank

Kirsimeti: Gobara ta lakume rayukan mutane 6

Date:

Gobara ta lakume rayukan mutane 6 ‘yan gida daya a lokacin da a ke bikin Kirsimeti a jihar Rivers.

Wani dattijo mai shekaru 70 mai suna, Pa Fidelis Ezinne wanda da ya tsallake rijiya da baya ya ce, wasu daga cikin wadanda abin ya shafa ‘ya’yansa ne da jikokinsa, inji rahoton Punch.

Lamarin ya faru ne a yankin Ngbede da ke karamar hukumar Ogba/Egbema/Ndoni a jihar Rivers, wadda ta yi sanadiyar mutuwar mutane shida ‘yan gida daya.

Likitan Septuagenarian ya ce, ya ji karar ne kawai daga wani janareta a daya daga cikin dakunan gidan da misalin karfe 6:30 na yamma.

“Ina zaune a waje kafin firiza na ya hura. Sai kuma abin da muka gani a gaba shi ne fashewar wani abu wanda ya raunata kowa.

 “Wannan ya kasance da misalin karfe 6:30 zuwa 7 na yamma. Kimanin mutane shida ne suka mutu -Dansa, matarsa ​​da yaronsa, ‘yar matata da kuma wani mutum guda.

 “Idan gwamnati na son taimakawa, su zo su taimake ni,” inji shi.

Wani ganau da a ka bayyana sunansa, Eric ya shaidawa SaharaReporters cewa, mai yiwuwa lamarin ya faru ne, sakamakon matsalar wutar lantarki inda a ka jona firij da na’urar kwantar da tarzoma.

 “Ina wajen gidan da ke kan hanya sai mu ka ji mutane suna kururuwa da wuta.

 “Kafin mu isa wurin, komai ya faru. Mun garzaya da wadanda abin ya shafa asibiti, amma ba su samu ba,” inji shi.

Da ya ke mayar da martani kan lamarin, Kwamandan wata kungiyar ‘yan banga mai suna OSPAC a yankin, Godknows Nkem, ya shawarci mazauna yankin da su yi taka-tsan-tsan wajen sarrafa kayan da a ke iya kamawa musamman ma wutar lantarki.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp