fidelitybank

Kiristoci ku zabi shugaban da zai kula daku a 2023 – Fasto Samuel

Date:

Fasto Samuel Oladele, Shugaban Cocin Apostolic Church (CAC), ya shawarci Kiristoci da su zabi ‘yan takarar da za su kare muradun su a babban zaben 2023.

Oladele ya ba da shawarar ne a cikin jawabinsa a taron 2022 Fastoci na CAC da aka gudanar a Ayo Babalola Memorial International Miracle Camp, Ikeji-Arakeji, Jihar Osun ranar Laraba.

Ya umurci Kiristoci su ƙyale amfanin Mulkin Allah ya ja-gorance su game da waɗanda za su zaɓa a babban zaɓe na gaba.

“Zaben gama gari mai zuwa shi ne wanda ya kamata mu yi sha’awar, domin ba za mu iya yin kasa a gwiwa ba yayin da ake yanke shawarar da ta shafi imaninmu.

“Za a yi mana jagora bisa ka’idojin da kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) ta tanadar domin zaben shugabannin siyasarmu na gaba a Najeriya.

“Ina ba da gaba gaɗi in shela da babbar murya cewa amfanin Mulkin Allah da na Kristinsa ya fi dukan sauran al’amura muhimmanci,” in ji shi.

Oladele ya koka da halin rashin tsaro da ake fama da shi a kasar, ya kuma bukaci ‘yan Najeriya da kada su yanke kauna, su kara yin addu’a da kuma tafiya a kan tafarkin adalci.

Malamin ya ba da tabbacin cewa akwai bege ga al’umma, ya kuma kara da cewa “Allah ne ke tafiyar da al’amuran mutane.”

vanguard 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp