fidelitybank

Kirga mutane zai kawo sauyi a Najeriya – Dr. Durunguwa

Date:

Kwamishinan kula da yawan jama’a na kasa, Dakta Abdulmalik Durunguwa, ya bayyana fatansa na ganin cewa, kidayar jama’a a shekarar 2023 za ta magance dimbin kalubalen da ke addabar kasar nan.

Da yake zantawa da manema labarai a ranar Juma’a a Abuja, ya bayar da tabbacin cewa, za a magance galibin matsalolin da ke addabar kasar idan an gudanar da kidayar jama’a sosai, yana mai cewa aikin zai nuna wa gwamnati hanyar da za ta bi wajen magance matsalolin.

A cewarsa, “kidayar za ta samar da bayanan da ake bukata ga gwamnati da abokan huldar ta don tsara yadda za a biya bukatun jama’a da kuma yadda za a dora kasar nan kan turbar ci gaba mai dorewa.”

Ya kara da cewa bayanan da ake bukata shine sanin inda mutum yake ba wai kauye ko jiha ba, yana mai jaddada cewa ainihin bayanan shine magance matsalolin mutane.

Ya bayyana cewa kasar na bukatar sanin abubuwan da suka hada da yadda al’ummarta ke ciki don haka ya kamata a kirga mutane a duk inda suke.

Ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su tabbatar an kidaya su domin gwamnati ta san mutanen da za su taimaka da yadda gwamnati za ta tsara.

Gwamnati, bayan kidayar, a cewarsa, za ta samu takardar aiki da za a yi amfani da ita wajen magance kalubale na musamman da ke shafar mutanen da ke zaune a sassan kasar.

nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp