fidelitybank

Kiran da gwamnan Zamfara ya yi na a rungumi makami bai dace ba – Janar Irabor

Date:

Babban hafsan tsaron kasa (CDS), Janar Lucky Irabor, ya caccaki kiran da Gwamna Bello Matawalle na jihar Zamfara ya yi kan al’ummar jihar cewa da su dauki makamai domin kare kansu daga ‘yan bindiga.

Irabor ya ce, kiran bai yi dai-dai ba, domin kuwa jami’an tsaro da sauran jami’an tsaro na can domin tunkarar kalubalen.

Irabor ya zanta da manema labarai kan lamarin a wajen bude taron hadin gwiwa na kwalejin tsaro ta kasa da kwalejojin yaki na rundunar sojin Najeriya mai lamba “Exercise Grand Nationale,” a Abuja.

Irabor ya ce, har yanzu bai fahimci dalilin da ya sa ‘yan jihar Zamfara su dauki makamai ba.

Sai dai ya ce hakki ne da ya rataya a wuyan Babban Lauyan Tarayya ya duba kundin tsarin mulki da dokoki don ganin ko gwamnan yana da irin wannan iko.

“Na yi imani cewa, a ganina, ba hanya ce da ta dace ba.

“Tabbas akwai ayyuka da jami’an tsaro da na sojoji, musamman ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro suke yi na magance tashe-tashen hankula a Zamfara da kewaye.

“Bayan haka, ko shakka babu, akwai wasu batutuwan shari’a, da sauran batutuwan da suka shafi mulki, batutuwan da gwamnati za ta iya magance su ta hanyar amfani da kayan aikin doka da aka tanadar masa domin samar da zaman lafiya da tsaro.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp