Akalla mutum 33 wadanda suka hada da mata da kananan yara ne ake tunanin sun mutu sakamakon kifewar wani kwale-kwale da ke dauke da fasinjoji fiye da 50 a kogin Kaduna a jihar Naija.
Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito cewa kwale-kwalen ya taso ne daga kauyen Danchitagi da ke karamar hukumar Lavun zuwa kauyen Gbara da ke karamar hukumar Mokwa a jihar ta Naija ranar Juma’a da daddare.
Rahotonni sun ruwaito cewa hatsarin ya faru ne sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya hade da iska mai karfin gaske.
Tuni dai aka dauki wadanda aka kubutar zuwa asibitin kauyen Gbara domin ba su kulawar gaggawa.
Hatsarin kwale-kwale dai na neman zama ruwan dare a Najeriya, ko a ranar Litinin din da ta gabata ma a ƙalla mutum 76 ne aka bayar da rahoton mutuwarsu bayan hatsarin kwale-kwale a jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Najeriya.
Kwale-kwalen, wanda ke É—auke da mutum 80, ya kife a yankin Ogbaru da ke jihar Anambran.
Mafi yawan wadanda abin ya rutsa da su mata ne da yara, da ke ƙoƙarin tsere wa yankinsu da ambliyar ruwa ta mamaye.