A kalla mutane uku ‘yan gida daya suka mutu a cikin mutane bakwai da su ka rasa ransu ta sanadiyar kifewar jirgin kwale-kwale a kauyen Zhigiri na karamar hukumar Shiroro da ke jihar Neja.
Jaridar Thisday, ta rawaito cewa, lamarin ya faru ne ranar Lahadi da maraice.
Cikin wadanda su ka mutu har da mata guda biyu na wani mutum mai suna Mallam Muazu Babangida da kuma dansa guda daya.
Sai dai ba a san sauran mutanen da suka mutu ba a hadarin.
Rahotanni sun nuna cewa, lamarin ya faru ne lokacin da mutanen suke kan hanyarsu ta zuwa kauyen Dnaweto, domin halartar bikin radin suna.
Sai dai kawo yanzu hukumomi ba su ce komai a kan batun, tun lokacin rubuta wannan labarin, sai dai sanarwar da kungiyar Coalition of Shiroro Association ta fitar ranar Talata ta tabbatar da faruwar lamarin.