Wani matashi, Tope Momoh, ya hallaka mahaifiyarsa ta hanyar tamke mata wuya saboda ta kira shi shege, a jihar Ondo ta Najeriya.
Matashin mai shekara 18 ya furta da bakinsa cewa shi ya hallaka mahaifiyar tasa mai shekara 52 mai suna Stella, mako biyu bayan an binne ta.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa, bayanai sun nuna cewa ya aikata ta’asar ne da tsakar daren 6 ga watan Satumba na wannan shekara ta 2022 a garin Ikakumi Akoko, na jihar ta Ondo.
Momoh, wanda aka gurfanar da shi a gaban babbar kotun majistare ta Akure ya masa laifin da aka tuhume shi da shi na kisa, amma kuma ya roki kotu ta tausaya masa.
Mai gabatar da kara, Nelson Akintimehin ya gaya wa kotun cewa ba a san sanadin mutuwar mahaifiyar matashin ba, kafin dan nata ya bayyana cewa shi ya kashe ta.