‘Yan sandan jihar Gombe ta damke wasu mutum 8 da aikata laifuka daban-daban a faɗin jihar.
Daya daga cikinsu, Garba Abubakar, a na zargin ya shake mahaifiyarsa har Lahira saboda ta masa fada ya daina mugayen hali.
Wani kuma ya yi lalata da ɗiyar makocinsa, wacce ke kai masa tallan abincin dabbobi yar shekara 10 kacal a duniya.
A ranar Laraba, hukumar y’an sanda reshen jihar Gombe ta jera wasu mutum takwas da ta kama da laifi daban-daban a faɗin jihar.
Jaridar The Nation ta rahoto cewa, ɗaya daga cikinsu, Garba Abubakar, ya shiga hannu ne bisa zargin kashe mahaifiyarsa, Salamatu Abubakar, yar shekara 45.