Rahotanni na nuni da cewar, an bar wasu iyalai a garin Iwo na jihar Osun cikin alhini bayan da har yanzu ba a san ko wanene ba sun kashe diyarsu, Shakirat.
Rahotannin da aka samu ga manema labarai sun bayyana cewa, wasu da ake zargin wasu mutane ne suka datsa sassan jikin matar.
Maharan da ake zargin yaran ‘Yahoo Yahoo’ ne (masu damfarar yanar gizo) sun jefar da gawar Shakirat a bayan shagon mahaifiyarta da ke Oke-Oore, inji rahoton Naija News Hausa.
Wani mazaunin unguwar da ya bayyana sunansa da Adeola ya shaida wa Daily Post cewa an gano gawar matar mai shekaru 22 da haihuwa da misalin karfe 8 na safe, inda ake zargin yaran Yahoo ne suka kashe ta.
An ce jami’an ‘yan sandan sun ziyarci inda lamarin ya faru inda suka kai gawar da aka yanka zuwa babban asibitin Iwo.
Kakakin rundunar ‘yan sanda Yemisi Opalola ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an fara gudanar da bincike, kamar yadda jaridar Naija News ta rawaito.