fidelitybank

Kayan cikin gida sun habaka da fiye da kashi 3 a Najeriya – NBS

Date:

Hukumar ƙididdiga ta kasa National Bureau of Statistics (NBS), ta ce, jumillar abin da Najeriya take samarwa da ake kira Gross Domestic Product (GDP) ya haɓaka da kashi 3.98 cikin 100 a wata ukun ƙarshe na 2021.

Wani rahoto da hukumar ta fitar a jiya Alhamis ya ce hakan na nuna cewa tattalin arzikin na kan hanyar da ta dace idan aka kwatanta da irin wannan lokacin na 2020.

“GDP ya haɓaka da kashi 3.98 cikin 100 cikin wata uku na karshe na 2021, abin da ke nufin alamun samun ci gaba a wata uku masu zuwa tun bayan annobar korona a 2020 lokacin da samar da kayayyaki ya yi ƙasa da kashi 6.10 da kuma 3.62 a wata uku na biyu da na ukun 2020 sakamakon annobar,” a cewar rahoton.

Ya ƙara da cewa “haɓakar na nuna alamun ci gaba da warwarewar tattalin arziki, inda ya kai kashi 3.40 a 20221”.

Kazalika, sakamakon na wata ukun ƙarshe a 2021 ya zarta na 0.11 da aka samu a irin wannan lokaci na 2020, sannan ya yi ƙasa da wanda aka samu a wata uku na uku a 2021 (maki 0.05).

Rahoton ya ce jumillar kayayyakin da ‘yan Najeriya ke samarwa ya zuwa wata ukun na ƙarshe a 2021 ya kai triliyan 49 – N49,276,018.23. In ji BBC.

nigeria newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp