fidelitybank

Kawai a soke wasan mu da Tottenham sai mu hakura – Liverpool

Date:

Kociyan Liverpool, Jurgen Klopp na son a sake wasan gasar Firimiya da ya gudana ranar Asabar tsakanin ƙungiyarsa ta Liverpool da Tottenham.

Tottenham ce ta yi nasarar cin 2-1 a karawar ta mako na bakwai da Liverpool ta kammala fafatawar da ‘yan kwallo tara a cikin fili.

Klopp ya bukaci a sake wasan ne bayan da alkalan da suka kula da na’urar VAR suka yi kuskuren soke kwallon da Luis Diaz ya ci, kan cewar an yi satar gida.

Darren England da Dan Cook ne suka kula da VAR a karawar da kungiyar Anfield ta ci gida daf da za a tashi ta hannun Joel Matip.

”Wani abu makamancin haka bai kamata ya faru ba a gasar Firimiya, saboda haka nake tunanin ya dace a sake wasan.” in ji Klopp.

To sai dai BBC ta fahimci cewar hukumar da ke kula da gasar ta Firimiya ba ta da wata madogarar da za ta amince a sake wasan, sannan babu tabbas ko Liverpool ta rubuta bukatar hakan a rubuce.

Wadanda suka tafka kuskuren a wasan na Tottenham da Liverpool ba sa cikin alkalan wasan da za su yi alƙalanci a wasannin gasar Firimiya da za a buga a karshen makon nan.

Inda aka bukaci England da Cook da su hutu, sakamakon kuskuren da suka tafka a karawar ta hamayya.

Wadanda suka hura wasan na Tottenham da Liverpool, Simon Hooper shi ne zai kula da VAR a fafatawar Bournmouth da za ta je gidan Everton ranar Asabar.

Shi kuwa Michael Oliver, wanda shi ne ya yi jiran ko-ta-kwana zai ja ragamar karawa biyu a karshen makon.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp