fidelitybank

Kawai a sake sabon zabe – PDP da LPD da kuma ADC

Date:

Jam’iyyun PDP, da LP da kuma ADC sun bukaci da a sake gudanar da sabon zaɓe, suna masu cewa zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar Asabar, inda suka ce zaɓen na cike da kura-kurai.

Shugaban Jam’iyyar PDP Iyorchia Ayu da sauran takwarorinsa na ADC Ralph Nwosu da Julius Abure na LP, sun bayyana haka ne a wani taron manema labarai da suka kira a Abuja yau Talata.

Jam’iyyun sun yi zargin cewa jami’an INEC sun tafka maguɗi a zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya da aka gudanar ta hanyar kin saka sakamakon zaɓen a shafin hukumar.

“Babu gaskiya a cikin wannan zaɓe, ana kuma ci gaba da soke sakamakon zaɓe a yankunan da jam’iyyun adawa ke da ƙarfi,” in ji Abure.

Sun kaɗa kuri’ar yankan kauna kan shugaban hukumar zaɓe farfesa Mahmood Yakubu, inda suka yi kira da ya gaggauta sauka domin wani ya maye gurbinsa da kuma gudanar da sabon zaɓe.

Jam’iyyun sun ce ba za su aminta da buƙatar saka sakamakon zaɓe a shafin hukumar zaɓe ba da shugabanta ya yi wanda kuma yake cikin sashi 60 na Dokar Zaɓe na 2022.

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp