Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta tabbatar da cewa, yanzu haka an taho da gawar Baturen ‘yan sandan karamar hukumar Jibia, DSP Abdullahi Rano, zuwa jihar Kano.
Majiyoyi a shelkwatar ‘yan sanda sun bayyana cewa, an tafi da gawarsa jihar Kano, domin yi masa jana’iza.
Mai magana da yawun ‘yan sandan jihar Katsina, SP Gambo Isah, ya yi alhinin mutuwar abokin aikinsa.
‘Yan bindiga sun hallaka Baturen ‘yan sanda da wani matashin hafsan Soja a garin Magamar Jibia.
Jami’in dan sandan ya rasa rayuwarsa ne yayin da ya jagoranci rundunar, domin dakile ‘yan bindigan da suka kai hari garin.
Jami’n Soja guda da ya samu rauni na kwance a asibiti, kuma an ce ya na murmurewa