fidelitybank

Katsina: Ba za mu bari sabuwar gwamnati ta gaji matsalar tsaro ba – Masari

Date:

Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari ya tabbatar da cewa yadda gwamnatin sa ta gaji matsalar tsaro a gwamnatin da ta gabata, insha Allahu ba za su yarda gwamnatin da za ta zo ta gaji matsalar ba.

Gwamna, Aminu Bello Masari ya bayyana hakan a yau Laraba 22-12-2021 a fadar gwamnatin jihar ta Janar Muhammadu Buhari, a lokacin da ya rattaba hannu a kan kasafin 2022.

Gwamnan ya kara da cewa”Duk da kalubalen tsaro da ake ta fuskanta tsawon lokaci da kuma irin kudaden da hakan ke ci, gwamnati ta yi iya kokarin ta wajen samar da ababen more rayuwa ga al’umma, musamman na karkara. wannan kasafin kudi ya maida hankali ne wajen kammala duk ayyukan da wannan gwamnati take kan yi, illa wasu kalilan masu muhimmanci da za a yi”.

“Aiwatar da wannan kasafin kudi sau da kafa ya na da matukar muhimmanci ga wannan gwamnati da kuma jam’iyyar APC, domin shi ne na karshe da za a aiwatar har zuwa karshen shekarar, na shekarar 2023”. Inji Masari.

Ya kuma yi kira ga ‘yan siyasa, musamman masu sha’awar yin takara, da su sa ni cewa Allah ba ya yin sabon aiki, duk wanda zai baiwa ya riga ya gama. Saboda haka wajibi ne ayi wannan hidima cikin bin doka da oda, tare da nuna ‘yan uwantaka domin samun nasarar jam’iyyar da kuma zaman lafiya da cigaban jihar.

Ya kuma yaba wa ‘yan majalisar saboda yadda su ka sadaukarwa da jajircewa wajen kammala tantance kasafin kudin cikin kwanaki talatin da biyar (35) da gabatar da shi a zauren majalisar.

Tun farko a nashi jawabin, shugaban majalisar dokokin jihar, Tasi’u Maigari Zango ya bayyana cewa, Majalisar ta yi nazari kwarai tare da tsantseni kan kasafin kudin, ta dalilin haka ne ma, ta gabatarwa wa Gwamnan Naira Biliyan Dari Ukku da Ashirin da Ukku, da Miliyan Dari Biyu da Tis’in da Shidda, da Dubu Dari Biyu da Ashirin da kuma Dari Shidda da Sittin da Daya(N323,296,220,961) kasa da Naira Biliyan Dari Ukku da Arba’in, da Miliyan Dari Tara da Hamsin da Daya da Dubu Dari Tara da Goma Sha Biyu da Dari Biyar Hamsin da Bakwai (N340,951,912,557) da tun farko Gwamnan ya gabatar a gaban zauren Majalisar.

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp