fidelitybank

Katsewar na’ura ya haifar da matsalar sadarwa a Najeriya da sauransu

Date:

Lalacewar wayoyin ƙarƙashin teku a sassan gabashi da yammacin Afirka lamarin ya sa ƙasashen Afirka da dama fuskantar gagarumar matsalar katsewar sadarwar intanet a ranar Alhamis.

Afirka ta Kudu da Najeriya da Ivory Coast da Laberiya da Ghana da Burkina Faso na cikin ƙasashen da suka fuskanci yankewar intanet ɗin.

Hukumar sadarwa ta Najeriya ta tabbatar da katsewar. Cikin wata sanarwa, NCC ta ce wayoyin da abin ya shafa sun taso ne daga Turai suka bi ta Gaɓar ruwan gashin Afirka.

Sun yanke ne a tekun maliya lamarin da ya shafi sauran wayoyin da ke haɗe da su a ƙarƙashin tekun.

“Kamfanonin wayoyin – WACS da ACE a gaɓar ruwan yammacin Afirka daga Turai sun fuskanci matsala.

NCC ta ƙara da cewa yankewar wayoyin ta sa an samu matsalar katsewar intanet a Najeriya da wasu ƙasashen yammacin Afirka sannan ƙarfin network na kamfanonin sadarwa ma ya fuskanci targarɗa a ƙasashen.

Shugaban ƙungiyar kamfanonin sadarwa a Najeriya Gbenga Adebayo ya tabbatar da matsalar da wayoyin ƙarƙashin tekun suka samu a tekun maliya.

MTN, ɗaya daga cikin manyan kamfanonin sadarwa a Najeriya ya fitar da sanarwa inda ya nemi afuwar abokan hulɗarsa saboda rashin ƙarfin network da suke fuskanta.

Shi ma ya ce hakan ta faru sakamakon lalacewar wasu sayoyin ƙarƙashin teku a sassan gabashi da yammacin Afirka.

Wasu bankuna a Najeriya suma sun nemi afuwar abokan hulɗarsu saboda matsalar da suka fuskanta. In ji BBC.

A Ivory Coast, ƙarfin sadarwar intanet ya ragu zuwa kashi huɗu cikin ɗari da safiyar ranar Alhamis a cewar Netblocks, kamfanin da ke bibiyar ƙarfin intanet.

A Laberiya ma ƙarfin intanet ɗin ya ragu zuwa kashi 17 cikin 100, a Benin kuma ya tsaya kan kashi 14 sai Ghana da kashi 25 kamar yadda Netblocks ya nuna.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp