fidelitybank

Katsewar na’ura ya haifar da matsalar sadarwa a Najeriya da sauransu

Date:

Lalacewar wayoyin ƙarƙashin teku a sassan gabashi da yammacin Afirka lamarin ya sa ƙasashen Afirka da dama fuskantar gagarumar matsalar katsewar sadarwar intanet a ranar Alhamis.

Afirka ta Kudu da Najeriya da Ivory Coast da Laberiya da Ghana da Burkina Faso na cikin ƙasashen da suka fuskanci yankewar intanet ɗin.

Hukumar sadarwa ta Najeriya ta tabbatar da katsewar. Cikin wata sanarwa, NCC ta ce wayoyin da abin ya shafa sun taso ne daga Turai suka bi ta Gaɓar ruwan gashin Afirka.

Sun yanke ne a tekun maliya lamarin da ya shafi sauran wayoyin da ke haɗe da su a ƙarƙashin tekun.

“Kamfanonin wayoyin – WACS da ACE a gaɓar ruwan yammacin Afirka daga Turai sun fuskanci matsala.

NCC ta ƙara da cewa yankewar wayoyin ta sa an samu matsalar katsewar intanet a Najeriya da wasu ƙasashen yammacin Afirka sannan ƙarfin network na kamfanonin sadarwa ma ya fuskanci targarɗa a ƙasashen.

Shugaban ƙungiyar kamfanonin sadarwa a Najeriya Gbenga Adebayo ya tabbatar da matsalar da wayoyin ƙarƙashin tekun suka samu a tekun maliya.

MTN, ɗaya daga cikin manyan kamfanonin sadarwa a Najeriya ya fitar da sanarwa inda ya nemi afuwar abokan hulɗarsa saboda rashin ƙarfin network da suke fuskanta.

Shi ma ya ce hakan ta faru sakamakon lalacewar wasu sayoyin ƙarƙashin teku a sassan gabashi da yammacin Afirka.

Wasu bankuna a Najeriya suma sun nemi afuwar abokan hulɗarsu saboda matsalar da suka fuskanta. In ji BBC.

A Ivory Coast, ƙarfin sadarwar intanet ya ragu zuwa kashi huɗu cikin ɗari da safiyar ranar Alhamis a cewar Netblocks, kamfanin da ke bibiyar ƙarfin intanet.

A Laberiya ma ƙarfin intanet ɗin ya ragu zuwa kashi 17 cikin 100, a Benin kuma ya tsaya kan kashi 14 sai Ghana da kashi 25 kamar yadda Netblocks ya nuna.

today nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp