fidelitybank

Katin Zabe: Tinubu ya yi amai ya lashe

Date:

Jagoran jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya yi amai ya lashe dangane da maganar da ya yi cewa wa’adin amfani da katin zabe ya kare, wato katin ya gama aiki.

A wata sanarwa da ofishin yada labarai na Tinubun ya fitar, ya ce, jagoran na su ya yi kuskuren ambaton kalmar karewa a Ingilishi wato ‘expire’ ne maimakon ya ce, ”kila akwai bukatar a sabunta katin.”

Sanarwar ta biyo bayan ce-ce-ku-cen da kalaman na Tinubu ne suka janyo har hukumar zabe ta Najeriya INEC, ta yi masa martani inda ta sheda wa BBC cewa wa’adin amfani da katin zaÉ“e bai Æ™are ba, za a ci gaba da amfani da shi wajen kaÉ—a Æ™uri’a.

Wani kwamishina ne a hukumar zaben bayan da BBC ta tuntube shi kan maganar ya faÉ—i hakan, bayan da wani bidiyo ya yaÉ—u a shafukan intanet da ke nuna Tinubu yana cewa wa’adin katin zaÉ“en ya Æ™are.

A cikin bidiyon an ga Bola Tinubu da takunkumi a fuskarsa kuma zagaye da mutane, ana jinshi yana cewa “wataÆ™ila ba za su gaya muku a kan lokaci ba… amma dai wa’adin amfani da katunan zaÉ“e ya Æ™are.”

Sai kuma Tinubu ya ci gaba da cewa: “kuna buÆ™atar yaÉ—a hakan a Æ™ananan hukumomi da mazaÉ“u komai wahalar yin hakan.”

A shekara ta 2021 ma a lokacin bikin cikar Asiwajun shekara 69 da haihuwa a Kano, jagoran na APC ya ce kamata ya yi a dauki matasa miliyan 50 a hukumomin tsaro na Najeriya domin shawo kan matsalar tsaro da ake fama da ita a kasar, amma kuma daga baya ya ce kuskure ya yi yana nufin dubu 50 ne, bayan da kalaman nasa suka tayar da kura.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naÉ—a shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp