fidelitybank

Katin Zabe: Tinubu ya yi amai ya lashe

Date:

Jagoran jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya yi amai ya lashe dangane da maganar da ya yi cewa wa’adin amfani da katin zabe ya kare, wato katin ya gama aiki.

A wata sanarwa da ofishin yada labarai na Tinubun ya fitar, ya ce, jagoran na su ya yi kuskuren ambaton kalmar karewa a Ingilishi wato ‘expire’ ne maimakon ya ce, ”kila akwai bukatar a sabunta katin.”

Sanarwar ta biyo bayan ce-ce-ku-cen da kalaman na Tinubu ne suka janyo har hukumar zabe ta Najeriya INEC, ta yi masa martani inda ta sheda wa BBC cewa wa’adin amfani da katin zaÉ“e bai Æ™are ba, za a ci gaba da amfani da shi wajen kaÉ—a Æ™uri’a.

Wani kwamishina ne a hukumar zaben bayan da BBC ta tuntube shi kan maganar ya faÉ—i hakan, bayan da wani bidiyo ya yaÉ—u a shafukan intanet da ke nuna Tinubu yana cewa wa’adin katin zaÉ“en ya Æ™are.

A cikin bidiyon an ga Bola Tinubu da takunkumi a fuskarsa kuma zagaye da mutane, ana jinshi yana cewa “wataÆ™ila ba za su gaya muku a kan lokaci ba… amma dai wa’adin amfani da katunan zaÉ“e ya Æ™are.”

Sai kuma Tinubu ya ci gaba da cewa: “kuna buÆ™atar yaÉ—a hakan a Æ™ananan hukumomi da mazaÉ“u komai wahalar yin hakan.”

A shekara ta 2021 ma a lokacin bikin cikar Asiwajun shekara 69 da haihuwa a Kano, jagoran na APC ya ce kamata ya yi a dauki matasa miliyan 50 a hukumomin tsaro na Najeriya domin shawo kan matsalar tsaro da ake fama da ita a kasar, amma kuma daga baya ya ce kuskure ya yi yana nufin dubu 50 ne, bayan da kalaman nasa suka tayar da kura.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faÉ—a ADC

Tsohon É—an jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

ÆŠan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buÆ™atun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...
X whatsapp