Jagoran jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya yi amai ya lashe dangane da maganar da ya yi cewa wa’adin amfani da katin zabe ya kare, wato katin ya gama aiki.
A wata sanarwa da ofishin yada labarai na Tinubun ya fitar, ya ce, jagoran na su ya yi kuskuren ambaton kalmar karewa a Ingilishi wato ‘expire’ ne maimakon ya ce, ”kila akwai bukatar a sabunta katin.”
Sanarwar ta biyo bayan ce-ce-ku-cen da kalaman na Tinubu ne suka janyo har hukumar zabe ta Najeriya INEC, ta yi masa martani inda ta sheda wa BBC cewa wa’adin amfani da katin zaÉ“e bai Æ™are ba, za a ci gaba da amfani da shi wajen kaÉ—a Æ™uri’a.
Wani kwamishina ne a hukumar zaben bayan da BBC ta tuntube shi kan maganar ya faÉ—i hakan, bayan da wani bidiyo ya yaÉ—u a shafukan intanet da ke nuna Tinubu yana cewa wa’adin katin zaÉ“en ya Æ™are.
A cikin bidiyon an ga Bola Tinubu da takunkumi a fuskarsa kuma zagaye da mutane, ana jinshi yana cewa “wataÆ™ila ba za su gaya muku a kan lokaci ba… amma dai wa’adin amfani da katunan zaÉ“e ya Æ™are.”
Sai kuma Tinubu ya ci gaba da cewa: “kuna buÆ™atar yaÉ—a hakan a Æ™ananan hukumomi da mazaÉ“u komai wahalar yin hakan.”
A shekara ta 2021 ma a lokacin bikin cikar Asiwajun shekara 69 da haihuwa a Kano, jagoran na APC ya ce kamata ya yi a dauki matasa miliyan 50 a hukumomin tsaro na Najeriya domin shawo kan matsalar tsaro da ake fama da ita a kasar, amma kuma daga baya ya ce kuskure ya yi yana nufin dubu 50 ne, bayan da kalaman nasa suka tayar da kura.