fidelitybank

Kasuwar Canji a Kano sun rufe shaguna saboda tsadar dala

Date:

Kungiyar yan canji a jihar Kano ta ce daga yanzu za ta rika bude kasuwar hada-hadar canji daga karfe 12 na rana zuwa 6 na yammacin kowace rana.

Yan canjin da ke kasuwar wapa sun dauki matakin rage lokutan da kasuwar ke ci a wani bangare na nuna fushi da yadda farashin dala ke ci gaba da hauhawa.

Kungiyar ta ce za ta ci gaba da yin haka ne har sai farashin dala ya sauka.

A baya kungiyar tana bude kasuwar ne da karfe 8 na safe zuwa 9 na dare.

A yayin da kungiyar yan canji a Abuja, babban birnin Najeriya ta dakatar da hada-hadar musayar kudi har sai baba ta gani sakamakon karancin dala.

Yan Najeriya dai sun dogara kacokan kan kudin Amurka – dala domin tafiyar da harkokin da suka shafi kudi.

Abdullahi Dauran, shugaban yan canji a Abuja, ya shaida wa BBC cewa sun dauki matakin ne domin nuna wa yan Najeriya cewa sun damu da yadda ake samun karancin dala matsalar da ya dora kan ayyukan kamfanin da ke hada-hadar kuÉ—aÉ—e ta Intanet irin na Crypto.

Lamarin na zuwa ne daidai lokacin da Babban bankin Najeriya ke kokari na daidaita kasuwar musayar kudaden waje.

Babban bankin ya umarci bankuna su sayar da dala yau Alhamis tare da gargadin mutane kan boye dalar domin samun riba.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp