fidelitybank

Kasuwar Canji a Kano sun rufe shaguna saboda tsadar dala

Date:

Kungiyar yan canji a jihar Kano ta ce daga yanzu za ta rika bude kasuwar hada-hadar canji daga karfe 12 na rana zuwa 6 na yammacin kowace rana.

Yan canjin da ke kasuwar wapa sun dauki matakin rage lokutan da kasuwar ke ci a wani bangare na nuna fushi da yadda farashin dala ke ci gaba da hauhawa.

Kungiyar ta ce za ta ci gaba da yin haka ne har sai farashin dala ya sauka.

A baya kungiyar tana bude kasuwar ne da karfe 8 na safe zuwa 9 na dare.

A yayin da kungiyar yan canji a Abuja, babban birnin Najeriya ta dakatar da hada-hadar musayar kudi har sai baba ta gani sakamakon karancin dala.

Yan Najeriya dai sun dogara kacokan kan kudin Amurka – dala domin tafiyar da harkokin da suka shafi kudi.

Abdullahi Dauran, shugaban yan canji a Abuja, ya shaida wa BBC cewa sun dauki matakin ne domin nuna wa yan Najeriya cewa sun damu da yadda ake samun karancin dala matsalar da ya dora kan ayyukan kamfanin da ke hada-hadar kuÉ—aÉ—e ta Intanet irin na Crypto.

Lamarin na zuwa ne daidai lokacin da Babban bankin Najeriya ke kokari na daidaita kasuwar musayar kudaden waje.

Babban bankin ya umarci bankuna su sayar da dala yau Alhamis tare da gargadin mutane kan boye dalar domin samun riba.

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haÉ—aka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...
X whatsapp