Kashi na shida na ‘yan Najeriya da aka kwashe daga kasar Ukraine sun isa filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja da yammacin ranar Asabar.
Sun isa a jirgin sama mallakar Azman Air. An dauke su ta jirgin sama daga kasar Hungary inda suka gudu bayan yakin Ukraine.
An kwashe ‘yan Najeriya 301 a cikin jirgin, wasu daga cikinsu dalibai ne da suka makale a birnin Sumy na kasar Ukraine da ya sha fama da hare-haren Rasha.
Mutanen da aka kwashe, a cewar hukumar ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje (NiDCOM), sun kuma samu katin SIM kyauta dauke da lokacin da za su iya kaiwa ga iyalansu. Katunan SIM ɗin sun kasance cikin haɗin gwiwa tsakanin NiDCOM da MTN, mai bada sabis na cibiyar sadarwa.
Wadanda aka kwashe sun kuma karbi dala 100 na sufuri kamar yadda ma’aikatan da suka iso gabansu suka samu.
PREMIUM TIMES ta ruwaito yadda a baya ‘yan Najeriya sama da 1,000 suka shigo daga kasar Ukraine. Mutanen da suka dawo sun tsere daga Ukraine zuwa kasashe makwabta kamar Poland da Hungary inda aka kai su Najeriya ta jirgin sama.
An kashe daruruwan mutane a Ukraine, tun bayan da Rasha ta mamaye kasar kimanin makwanni biyu da suka gabata yayin da sama da mutane miliyan biyu suka rasa matsugunansu.