Kashi na biyar na ‘yan Najeriya da aka kwashe daga kasar Ukraine sun isa filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja da sanyin safiyar Juma’a.
Sun isa ne a cikin wani jirgin sama mallakin Air Peace, daya daga cikin kamfanonin jiragen da aka biya kudin jigilar ‘yan Najeriya da suka dawo daga Ukraine. An dauke su ta jirgin sama daga Poland inda suka gudu bayan yakin Ukraine.
An kwashe ‘yan Najeriya 123 a jirgi na biyar, a cewar gwamnatin tarayya.
Mutanen da aka kwashe, a cewar hukumar ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje (NiDCOM), sun kuma samu katin SIM na kyauta wanda aka yi ma su da lokacin isar da sako domin su samu damar isa ga ‘yan uwansu ta hanyar hadin gwiwa tsakanin NiDCOM da MTN.
Wadanda aka kwashe sun kuma karbi dala 100 na sufuri kamar yadda ma’aikatan da suka iso gabansu suka samu.
A ranar Asabar ne ake sa ran wani rukunin zai isa Najeriya daga kasar Hungary, kamar yadda wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fitar.
PREMIUM TIMES ta ruwaito isar mutane 1,078 da suka isa Najeriya a makon da ya gabata ta hanyar Max Air da Air Peace, kamfanonin jiragen biyu sun dauki nauyin jigilar ‘yan Najeriya da suka dawo daga Ukraine.