fidelitybank

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na ƙarƙashin ƴan Bindiga – Ɗan majalisa

Date:

Rahotanni daga yakin ƙaramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara da ke arewacin Najeriya, sun ce ƴanbindiga sun kashe jami’an da ke samar da tsaro goma sha uku (13) a cikin mazabar Adabka, yayin da suke tsaka da gudanar da sintiri.

Harin wanda ƴanbindigar suka kai a jiya Juma’a, sannan suka ƙi bari a shiga domin a kwaso gawarwakin jami’an da suka kashe domin yi musu sutura.

Hamisu A Faru, shi ne ɗan majalisar jihar, mai wakiltar Bukuyum ta Kudu, a zantawarsa da BBC ya buƙaci gwamnatin tarayya ta gaggauta kai musu ɗauki, bisa la’akari da girman matsalar.

Ya ce al’ummar mazaɓarsa na cikin tashin hankali, “musamman ganin waɗanda suke taimaka musu wajen ba su kariya ne aka kashe. Ka ga ke nan me ya rage? ai sai gudun hijira, dama tuni wasu sun gudu zuwa Zuru.”

Ɗan majalisar ya ƙara da cewa kashi 70 na mazaɓar Bukuyum ta Kudu, a ƙarƙashin mulkin ƴanbindiga yake.

A ƙarshe ya yi kira ga gwamnatin tarayya ta tura jiragen yaƙi a shiga dazukan, “a yi luguden wuta sansanonn ƴanbindigar.”

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp