fidelitybank

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na ƙarƙashin ƴan Bindiga – Ɗan majalisa

Date:

Rahotanni daga yakin ƙaramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara da ke arewacin Najeriya, sun ce ƴanbindiga sun kashe jami’an da ke samar da tsaro goma sha uku (13) a cikin mazabar Adabka, yayin da suke tsaka da gudanar da sintiri.

Harin wanda ƴanbindigar suka kai a jiya Juma’a, sannan suka ƙi bari a shiga domin a kwaso gawarwakin jami’an da suka kashe domin yi musu sutura.

Hamisu A Faru, shi ne ɗan majalisar jihar, mai wakiltar Bukuyum ta Kudu, a zantawarsa da BBC ya buƙaci gwamnatin tarayya ta gaggauta kai musu ɗauki, bisa la’akari da girman matsalar.

Ya ce al’ummar mazaɓarsa na cikin tashin hankali, “musamman ganin waɗanda suke taimaka musu wajen ba su kariya ne aka kashe. Ka ga ke nan me ya rage? ai sai gudun hijira, dama tuni wasu sun gudu zuwa Zuru.”

Ɗan majalisar ya ƙara da cewa kashi 70 na mazaɓar Bukuyum ta Kudu, a ƙarƙashin mulkin ƴanbindiga yake.

A ƙarshe ya yi kira ga gwamnatin tarayya ta tura jiragen yaƙi a shiga dazukan, “a yi luguden wuta sansanonn ƴanbindigar.”

labaran duniya na yau

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na ƙarƙashin ƴan Bindiga – Ɗan majalisa

Rahotanni daga yakin ƙaramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara...

Goodluck ya fi dacewa ya zama dan takara a 2027 – Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya ce Tsohon...

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...
X whatsapp