fidelitybank

Kashi 63 na ‘yan Najeriya matalauta ne – Gwamnati

Date:

Gwamnatin ta bayyana cewa, kashi 63 cikin 100 na ƴan ƙasa, wato mutum miliyan 133 na cikin talauci.

Alƙaluman binciken ma’aunin talauci a Najeriya ne suka tabbatar da hakan a yau Alhamis a Abuja.

Hukumar ƙididdiga ta ƙasa da hukumar tsara bayar da tallafi ga masu ƙaramin ƙarfi da shirin samar da ci gaba na majalisar ɗinkin duniya da asusun ilimin ƙanana yara na Unicef da shirin yaƙi da talauci da cigaban al’umma na Oxford ne suka gudanar da aikin ƙididdigar.

Binciken ya nuna cewa an karɓi bayanan magidanta dubu 56 a sassan jihohin ƙasar 36 da birnin tarayya Abuja, da aka gudanar tsakanin watan Nuwamban 2021 zuwa Fabarairun 2022.

Bayanan da aka tattara sun nuna cewa kashi 65 cikin 100 na matalauta a ƙasar na rayuwa ne a arewacin Najeriya, yayin da kashi 35 cikin 100, kusan mutum miliyan 47 ke nan na zama ne a kudanci.

Sokoto ce jihar da ta fi fama da talauci a ƙasar, inda kashi 91 cikin 100 na al’ummarta ke rayuwa hannu-baka hannu-ƙwarya, Ondo ce kuma mafi ƙarancin talauci a Najeriya da kashi 27 cikin 100.

A lokacin da ya yi tsokaci kan alƙaluman, Shugaba Muhammadu Buhari ya ce wannan bayani zai bijiro da hanyoyin da za a bi wajen yaƙi da talauci.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...

An gargadi Borno da Yobe da Jigawa su zama cikin shirin ambaliya

Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da...

Kano na cikin jihohin da ba su yi katin zabe sosai ba – INEC

Bayanan da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya...

Mun gano filin wasa na Sani Abacha ba shi da inganci – NPFL

Hukumar shirya gasar cin kofin kwararru ta kasa (NPFL),...

Jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna ya ya fadi

Jirgin ƙasa ɗauke da fasinjoji da ya taso daga...

Jami’in mu bai saci naira biliyan 6.5 ba – Gwamnatin Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta karyata rahoton da ya zargi...

Gwamnatin Kano ta gargadi Matasa da ‘yan Gwangwan kan sayen kayan gwamnati

Gwamnatin Jihar Kano ta gargadi matasa da ’yan kasuwa...

NIMET ta gargai Borno kan ambaliya da sauran jihohi

A baya-bayan nan ne hukumar hasashen yanayi ta Najeriya...

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...
X whatsapp