fidelitybank

Kashi 50 na Matan Najeriya ba sa zuwa makaranta – UNICEF

Date:

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, ya ce sama da kashi 50 cikin 100 na ‘yan mata a Najeriya ba sa zuwa makaranta.

Jutaro Sakamoto, manajan ilimi a UNICEF ne ya bayyana haka a Abuja a wajen taron ilimi da Cibiyar Faransa a Najeriya ta shirya.

Ya ce ƴan mata miliyan 7.6 ba sa zuwa makaranta a Najeriya – miliyan 3.9 a matakin firamare yayin da miliyan 3.7 kuma a matakin karamar sakandare.

Sakamoto ya kuma ce kashi 48 cikin 100 na ‘yan matan da ba sa zuwa makaranta, suna fito ne daga yankin Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabas.

A cewarsa, kashi 9 cikin 100 na ‘yan mata masu fama da talauci suna zuwa makarantar sakandare, idan aka kwatanta da kashi 81 cikin 100 na waɗanda suka fito daga gidajen masu hannu da shuni.

Yayin da yake mayar da martani kan cewa Najeriya ce ke da kashi 15 cikin 100 na yaran da ba sa zuwa makaranta a duniya, Sakamoto ya ce, “Idan ba za mu iya magance halin da ake ciki a Najeriya ba, ba za mu iya magance matsalar a duniya ba.”

Ya ce ba a koyar da waɗanda suke zuwa makaranta yadda ya kamata, sakamakon rashin kayan aiki.

Ya ce shirin da UNICEF ta samar, ya taimaka wa yaran da ba sa zuwa makaranta tun da farko ta hanyar ba su ilimi mai nagarta.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp