Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, ya ce sama da kashi 50 cikin 100 na ‘yan mata a Najeriya ba sa zuwa makaranta.
Jutaro Sakamoto, manajan ilimi a UNICEF ne ya bayyana haka a Abuja a wajen taron ilimi da Cibiyar Faransa a Najeriya ta shirya.
Ya ce ƴan mata miliyan 7.6 ba sa zuwa makaranta a Najeriya – miliyan 3.9 a matakin firamare yayin da miliyan 3.7 kuma a matakin karamar sakandare.
Sakamoto ya kuma ce kashi 48 cikin 100 na ‘yan matan da ba sa zuwa makaranta, suna fito ne daga yankin Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabas.
A cewarsa, kashi 9 cikin 100 na ‘yan mata masu fama da talauci suna zuwa makarantar sakandare, idan aka kwatanta da kashi 81 cikin 100 na waɗanda suka fito daga gidajen masu hannu da shuni.
Yayin da yake mayar da martani kan cewa Najeriya ce ke da kashi 15 cikin 100 na yaran da ba sa zuwa makaranta a duniya, Sakamoto ya ce, “Idan ba za mu iya magance halin da ake ciki a Najeriya ba, ba za mu iya magance matsalar a duniya ba.”
Ya ce ba a koyar da waɗanda suke zuwa makaranta yadda ya kamata, sakamakon rashin kayan aiki.
Ya ce shirin da UNICEF ta samar, ya taimaka wa yaran da ba sa zuwa makaranta tun da farko ta hanyar ba su ilimi mai nagarta.