Hukumar zabe ta kasa INEC, ta bayyana kashi 42 cikin 100 na sabbin rajistar masu kada kuri’a a matsayin mara inganci a daidai lokacin da ta kaddamar da sabbin katunan zabe na dindindin (PVCs), domin rabawa a fadin kasar.
Hukumar ta bakin shugabanta na kasa Mahmood Yakubu, a ranar Larabar da ta gabata, ta ce, jimlar PVC guda 1,854,859 za a shirya domin karbar su kai tsaye a jihohi 36 da babban birnin tarayya Abuja bayan hutun Ista.
Tun bayan fara rijistar masu kada kuri’a ta ci gaba da yi (CVR) a ranar 28 ga watan Yuni, 2021, miliyoyin ‘yan Najeriya sun kammala yin rijistar da kuma internet gabanin babban zaben 2023.
Daga cikin wadannan alkaluman da aka bazu a cikin kashi hudu, Yakubu ya ce, sama da kashi 55 cikin 100 na mahalarta taron a watan Yuni da Disamba 2021 sun samu ta hanyar tsaftace bayanan hukumar.
Ya bayyana yawan rajistar da kuma rashin cika bayanai a matsayin dalilan da suka haddasa rashin yin rajistar masu kada kuri’a, ‘ba bisa ka’ida ba, ya bayyana cewa, wasu ma’aikatan hukumar a fadin kasar nan sun karfafa musu gwiwa.