fidelitybank

Kashi 20 na ‘yan Afrika na fama da matsalar yunwa – Majalisar Dinkin Duniya

Date:

Wani sabon rahoton da cibiyoyin Majalisar Dinkin Duniya da hadin gwiwar ƙungiyar Afirka, sun ce ‘yan Afirka miliyan 282, kusan kashi 20 na al’ummar nahiyar ne ke fama da matsalar ƙarancin abinci.

Rahoton haɗin gwiwar ya kuma nuna cewa yawan mutanen da ke fama da ƙarancin abinci sun ƙaru da miliyan 57 tun bayan ɓarkewar cutar covid, lamarin da ya haifar da taɓarɓarewar matsalar abinci a nahiyar.

“Mafi yawan al’ummar Afirka – kusan kashi 78 ko fiye da mutum biliyan guda – ba sa samun lafiyayen abinci, idan aka kwatanta da kashi 42 da ke samun hakan a faɗin duniya, kuma adadin na ci gaba da ƙaruwa,” in ji rahoton.

Rahoton ya kuma alaƙanta rashin samun lafiyayen abincin kan matsalar ƙarancin abinci da aka fuskanta a ‘yan shekarun baya-bayan nan, musamman a Yammaci da Gabashin Afirka, wanda ya sa ba ma talakawa kaɗai ba, har ma da masu dama-daman ba sa iya samun lafiyayyen abinci.

Hukumomin sun kuma ce kusan kashi 30 na ƙananan yara ‘yan ƙasa da shekara biyar ne a nahiyar suka takure sakamakon rashin samun ingantaccen abinci.

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp