Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya ce, mutuwar shugaban Hamas, Yahya Sinwar, a ranar Laraba, ba ta nufin kawo karshen yaƙin Gaza.
Mutumin wanda aka yi imanin shi ne ya kitsa harin 7 ga watan Oktoba da ya janyo mutuwar sama da mutum 1,200 a Isra’ila, ya mutu ne sakamakon farmakin da sojojin Isra’ila suka kai masa a Rafah da ke kudancin yankin.
Mista Netanyahu ya ce mutuwar Sinwar za ta sa haske ya mamaye duhu a gabas ta tsakiya.
Sai dai ya dage cewa Isra’ila za ta ci gaba da fafatawa da dukkan karfinta har sai ta ceto yan ƙasar da Hamas ke riƙe da su.
Zuwa yanzu dai babu wani martani daga ƙungiyar ta Hamas game da wannan batu.