fidelitybank

Kashe Kudade: Majalisa ta gayyato hukumomin gwamnati 63

Date:

Kwamitin Majalisar wakilai da ke sa ido kan yadda ake kashe kuɗaɗen gwamnati ya gayyaci ma’aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya 63, domin bayar da bahasi game da aiwatar da wasu ayyukan da ba sa cikin kasafin kuɗin da shugaban ƙasar ya gabatar a gaban majalisar, abin da kwamitin ya ce ya haddasa kashe kuɗi ba bisa ƙa’ida ba da yawansu ya kai sama da tiriliyan biyu.

Shugaban kwamitin Oluwole Oke, ya rubuta wasiƙa zuwa ga babban daraktan hukumar kasafin kuɗi ta ƙasar yana mai bayyana buƙatar neman hujjar majalisar wakilan kasar kan yin hakan.

Shugaban ƙasa ne ke miƙa kasafin kuɗin ma’aikatu ga hukumomin gwamnatin zuwa ga majalisar wakilan ƙasar, yayin da Akawun majalisar zai mayar wa shugaban kasar kasafin da majalisar ta amince da shi domin aiwatarwa.

Yayin da yake ƙarin haske kan wasiƙar mista Oke ya ce ”An kashe sama da tiriliyan biyu ba bisa ƙa’ida ba. Shugaban ƙasa bai kawo kasafin kuɗinsu ba. Dole su faɗa wa ‘yan Najeriya me yasa suke aiwatar da kasafin kuɗin da bai bi matakan shari’a ba”.

”Shugaban ƙasa bai gabatar da kasafinsu a majalisa ba. Haka kakakin majalisa da shugaban majalisar dattawa ba ɗaya daga cikinsu da ya gabatar da wannan batu a harabar majalisun dokokin ƙasar biyu. Dan haka mun gayyaci hukumomin da su zo su yi bayani”, in ji shi.

punch newspaper headlines today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...

Rikicinta da Cambodia na iya rikidewa ya koma yaƙi – Thailand

Thailand ta gargaɗi cewa rikicinta da Cambodia na iya...

Isra’ila da Amurka sun soki Faransa na amincewa da kafuwar ƙasar Falasɗinawa

Isra'ila da Amurka sun yi Allah-wadai da matakin da...

Najeriya za ta kwashe ma’aikatan ta a Congo – Tugar

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, ta na shirin kwashe...

Ministan harkokin jin ƙai ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa

Ministan harkokin jin kai, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya zama...

Amurka za ta lalata magungunan takarar haihuwa na dala miliyan 10 da za a kawo Afrika

Gwamnatin Amurka na shirin lalata magungunan tazarar haihuwa da...

Hukumar NAFDAC ta kama abubuwan fashewa a Kano

A cewar hukumar, an gano lita 60,000 na sulphuric...

Sojoji sun fafata da da ‘yan Bindiga a Neja

Rundunar sojiji ta ce, sojoji tare da haɗin gwiwar...
X whatsapp