Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje, ya ce, shugabannin kasashen Nijar, Kamaru, Chadi da Afirka ta tsakiya, sun nuna sha’awarsu na bayar da cikakken goyon baya ga aikin na biliyoyin Naira bayan kaddamar da shi.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnan, Abba Anwar, ya rabawa manema labarai a Kano ranar Asabar.
A cewar Anwar, Ganduje ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kai ziyarar tantance ma’aikatar a ranar Juma’a, inda shugaban tashar tsandaurin, Sahabo Abubakar Bawuro, da Manajan Daraktan, Ahmed Rabi’u suka zagaya da shi.
“Dukkan shugabannin jamhuriyar Nijar, Chadi, Kamaru da Afirka ta Tsakiya, sun nuna sha’awarsu da shirye-shiryensu na amfani da tashar Tsandauribn ta Kano wajen shigo da su da kuma fitar da su,” in ji Ganduje.
Ya ce, shuwagabannin kasashen hudu duk sun amince za su wuce Kano su tura jami’ansu, domin su zo su tattauna da hukumomi kan tsarin tafiyar da sabuwar tashar ruwan busasshiyar kafin kaddamar da shi.
Ya yi kira ga masu son zama manajojin tashar jiragen ruwa da su tabbatar sun gudanar da komai ta hanyar zamani.