fidelitybank

Kasashe 5 sun nuna fargabar kai hari Abuja

Date:

Ƙarin ƙasashe biyar sun bi sahun Amurka da Birtaniya wajen bayyana fargabar kai harin ta’addanci a Abuja, tun daga ƙarshen makon da ya gabata, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Amurka ce ta fara bayyana damuwa a ranar Lahadi, tana mai cewa akwai yiwuwar kai hari kan gine-ginen gwamnati da wuraren taruwar jama’a, kafin a ranar Juma’a ta umarci wasu ma’aikatan difilomasiyyarta su fice daga binin tare da iyalansu nan take.

Jim kaɗan bayan haka Ofishin Harkokin Waje na Birtaniya ma ya gargaɗi ‘yan ƙasarsa da su ankare kuma su guji yawo a Abuja tare da kauce wa shiga taron jama’a.

Ƙasashen Jamus da Bulgeriya da Ireland da Kanada da Denmark sun bi sahu, inda suke cewa akwai yiwuwar ‘yan ta’adda za su kai hare-hare sannan suka nemi ‘yan ƙasashensu su yi taka-tsantsan ko kuma su fice daga birnin.

Sai dai Babban Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya IGP Usman Alkali Baba ya jaddada cewa babu wata fargabar kai hare-hare a Abuja, bayan ya umarci jami’ansa da su tsaurara tsaro a kewayen Abuja.

“Saboda haka IGP na kwantar wa da mazauna Abuja hankali tare da ƙarfafa musu gwiwar ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum yayin da aka shirya tsafi don daƙile barazanar tsaro da kuma amsa kiran gaggawa a kan lokaci,” in ji sanarwar da kakakin ‘yan sandan ya fitar ranar Alhamis.

sun newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...
X whatsapp