fidelitybank

Kasar Masar ta hana daliban Najeriya ketare iyakar ta

Date:

Hukumar kula da ƴan Najeriya mazauna ƙasashen ƙetare, ta ce hukumomin Masar sun ƙi buɗe kan iyakarsu ga ɗaliban Najeriya waɗanda ke guje wa rikicin da ke faruwa a Sudan.

Sai dai hukumar ta ce yanzu haka akwai jirgin sojin Najeriya da ke girke a birnin Aswan, kuma a cewar ta, jirgin ba zai baro birnin ba sai ya ɗauki ɗaliban na Najeriya.

Har yanzu dai Najeriya na fafutikar ganin yadda za ta iya kwaso dubban ɗalibai da sauran al’ummarta daga Sudan inda faɗa ya ɓarke a makon jiya.

Bayanai na cewa wasu ɗaliban na kan hanyarsu ta zuwa kan iyakar Sudan da Saudiyya, inda ake sa ran za su tsallaka zuwa cikin ƙasar kafin a kwashe su zuwa gida.

Faɗa ya ɓarke ne tsakanin ɓangarorin dakaru masu biyayya da manyan jami’an sojin Sudan biyu.

Tuni ƙasashe da dama suka kwashe al’ummarsu domin gudun kada yaƙin ya rutsa da su.

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp