fidelitybank

Kasa ta rufta da yara 8 a jihar Kebbi

Date:

Kimanin yara takwas sun mutun bayan ƙasar gini ta rufta musu a mahaƙar ƙasar ginin ta Dustin Dukku da ke unguwar Badariya a ƙaramar hukumar Birnin Kebbi a jihar Kebbi.

Shugaban ƙaramar hukumar Hon. Muhammad Dahiru Ambursa, ya tabbatar wa da BBC faruwar lamarin, inda ya ce tuni aka fara shirye-shiryen yi wa yaran jana’iza.

Ya kuma ce akwai wasu ƙarin yara biyu da suka jikkata ciki har da wanda ya karye a ƙafa.

To sai dai wani mutum da abin ya faru a gaban idonsa ya shaida wa BBC cewa yara tara ne suka rasu, lokacin iftila’in da ya faru da safiyar ranar Asabar

Shugaban karamar hukumar ya ce mafi yawa daga cikin yaran da lamarin ya rutsa da su almajirai ne waɗanda ke aikin haƙar ƙasar gini a yankin.

Honarabul Ambursa ya ce ya bayar da umarnin dakatar da haƙar ƙasar gini a wurin.

”Mun bayar da umarnin killace wurin da waya tare da saka alamar da ke nuna cewa an hana haƙar ƙasar gini a wurin, mun kuma buƙaci hakimai da sauran iyayen ƙasa da su saka a yi shela, don hana mutane haƙar ƙasar gini a wannan wuri”, in ji shi.

Masu ƙaramin ƙarfi dai kan yi amfani da ƙasa wajen yin bulon ƙasa da za su yi amfani da shi wajen yin gine-ginen musamman a garuruwa da ƙauyuka a Najeriya.

guardian newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp