Majalisar kamfen din jamâiyyar APC reshen jihar Yobe, a ranar Lahadi, ta musanta rahotannin da ke cewa an kai wa Gwamna Mai Mala Buni hari a karamar hukumar Gashua ta jihar.
Rahotanni sun bayyana cewa wasu fusatattun matasa sun jefe Buni da duwatsu a yayin wani gangami a garin Gashua a ranar Asabar.
Babban daraktan yakin neman zaben (DG), Sen. Mohammed Hassan, ya yi wannan martani a wani taron manema labarai a Damaturu.
Karanta Wannan:Â Buni ya mika ta’aziya ga mutae 3 da suka mutu a hanyar Bauchi
Ya ce, âbabu wani abu kamar jifa kamar yadda wani sashe na kafafen yada labarai suka ruwaito.
âZan iya gaya muku cewa ba a taba ganin irin fitowar jamaâa a wurin taron ba, kuma jamaâa daga koâina suka zo domin marawa jamâiyyar baya, gwamnanmu da nasarorin da ya samu.
Shima da yake magana, Mamman Mohammed, Darakta-Janar na Yada Labarai da Harkokin Watsa Labarai ga Buni, ya bayyana cewa yana bukatar mayar da martani ga “rahoton karya, mai ban tsoro da rashin fahimta don gujewa yaudarar jama’a”.