fidelitybank

KAROTA ta kama mai ƙwacen waya a babur

Date:

Hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Kano KAROTA, ta cafke wani mai tuƙa babur ɗin Adaidaita sahu Yusuf Abdurrahman Ƙwaya bisa zargin sa da satar wayoyin mutane a babur ɗinsa.

Hakan na cikin wata sanarwa da jami’’in hulɗa da jama’a na hukumar Nabilusi Abubakar Ƙofar Na’isa ya raba wa manema labarai da yammacin yau Litinin.

Sanarwar ta ce, jami’an hukumar ne suka cafke matashin a kan Titin Yan kaba.

saƙon murya da jami’i ya raba wa manema labarai ya ce,, Yusuf Abdurrahman mai laƙabin Ƙwaya da aka cafke shi bisa zargin satar wayoyin ya ce, “Ba ƙwace muke yi ba kwai ƴan dabaru muke yi wajen ɗaukar wayoyin”.

“Wani lokacin muna yaudarar mutane da cewa za mu sayi ruwan sha ko kuma mu yi musu wata dabarar, wannan shi ne karo na biyu da aka taɓa kama ni ana kawo ni hukumar KAROTA” Inji shi.

Ɗaya daga cikin waɗanda aka ɗauke wa waya Malam Rabi’u Ya’u ya shaida wa hukumar ta KAROTA cewa, “Na hau babur ɗin ɓata garin ne daga tashar ƴan Kaba, kuma bayan ya hau ne sai abokin tafiyar direban ya sauya mazauni daga kusa da shi zuwa gaban baburin kusa da direba”.

“Ashe ban sani ba tun lokacin da ya sauya wurin tuni ya sace mun waya, don haka da suka tsaya zan sauka ba su tsaya na ba su kuɗi ba suna ta sauri sai da kyar na ba su, daga nan ne ban ga waya ta ba, don haka na yi ta kiranta m, sai dai daga bisani aka ɗaga tare da faɗa mun na zo gidan KAROTA na karɓa an kama su”.

Haka kuma sanarwar ta ruwaito cewa tuni hukumar ta miƙa Yusuf Ƙwaya ga rundunar ƴan sanda ta jihar Kano domin faɗaɗa bincike tare da wayoyin da aka cafke shi da su guda shida. In ji jaridar Kakaki.

today nation

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp