Kamfanin zirga-zirgar jiragen sama na Qatar Airways, ya fara sauka a birnin Kano a yau Laraba cikin murna da annashuwa daga hukumomin ƙasar da kuma kamfanin.
Jirgin Boeing 787 ya sauka a babban filin jirgi na Mallam Aminu Kano (MAKIA) da misalin ƙarfe 11:00 da ɗoriya.
Jekadan Najeriya a ƙasar Qatar, wadda ta mallaki kamfanin, Ahmadu Yakubu Abdullahi na cikin waɗanda suka halarci bikin saukar jirgin karon farko a tarihi.
Kano ce, wuri na uku a Najeriya da kamfanin zai rinka sauka, bayan Abuja da Legas.
A gobe Alhamis kuma zai ƙarasa birnin Fatakwal na Jihar Rivers da sauran su.