Ma’aikatan gwamnati a jihar Kwara na cike da farin ciki, bayan da gwamnatin jihar ta kammala aiwatar da mafi karancin albashin ma’aikata na kowane bangare na ma’aikatanta, tare da karfafa karfin siye da kuma farfado da tattalin arzikin kananan hukumomi.
Albashin watan Janairu a ranar Litinin da gwamnatin ta biya, ya jawo yabo ga gwamna Abdulrahman Abdulrazaq, saboda cika alkawarin da ya yi na aiwatar da sakamakon gyara bangaren mafi karancin albashi a yayin da ake kara raguwa.
Da yake jinjinawa wannan karimcin da gwamnatin ta yi, sakataren kungiyar ta hadin gwiwa ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa, wannan ci gaban abin a yaba ne, kuma gwamnan ya cancanci a yi masa maraba.
“Kungiyar Kwadago ta jihar Kwara a karkashin TUC, NLC da JNC na fatan yin amfani da wannan kafa wajen mika godiya ga gwamnatin jihar Kwara, karkashin jagorancin, Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq, bisa kishin kasa kan wannan gagarumar nasara da muka samu. wannan lokaci na tattalin arzikinmu da na kudi wanda ya shafi kowane bangare na kokarin dan Adam,” in ji Sakataren JNC Kwamared Tunde Meshach Joseph a cikin sanarwar.
“A kan wannan bayanin ’yan uwa, ya zama wajibi mu yaba wa ma’aikatan Jihar Kwara bisa jajircewarku, aminci, goyon bayanku da addu’o’in ku a cikin wadannan shekaru, muna cewa mun gode.