Hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC, ta bayyana damuwa cewa, ƙarancin man fetur da ake fama da shi a ƙasar na iya shafar shirye-shiryen babban zaben da za a yi ranar 25 ga watan Fabrairu.
Dogayen layuka a gidajen sayar da man fetur sun zama kamar jiki a fadin ƙasar, musamman a Legas baban birnin kasuwanci na ƙasar, inda ‘yan Najeriya kan shafe sa’o’i kafin su sayi man.
Miliyoyin ‘yan ƙasar sun dogara da makamashin fetur ne, ba domin sufuri kawai ba, har domin tayar da jannareto doimn samar da lantarki a gidaje da wuraren sana’arsu.
Farashi wannan makamashin ya yi tashin goron zabi cikin watannin da suka gabata, har ta kai ga farashin fetur ya ninka a kasuwannin bayan fage.
Gwamnatin ƙasar ta musanta cewa an yi ƙarin farashin albarkatun mai, kuma ta ce akwai isassun albarkatun a cikin ƙasar.
Sai dai ta dora alhakin ƙarancin man kan ‘yan kasuwa wadanda ke da alhakin sayar da man ga al’ummar ƙasar a yawancin gidajen mai, tana cewa su ne suke janyo matsalolin da ake fuskanta.