Gwamnatin tarayya ta mayar da martani ga ikirari da kungiyar dillalan man fetur mai zaman kanta ta kasa (IPMAN) reshen Suleja, sakamakon rashin biyan kudaden da ake yi na hada-hadar man fetur, inda ta bayyana cewa, ta biya Naira biliyan 74 kamar yadda ikirari da ‘yan kasuwar man suka yi.
An bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Mista Kimchi Apollo, Janar Manaja, Kamfanin Sadarwa na Kamfanin, Nigerian Midstream and Downstream Petroleum Regulatory Authority (NMDPRA) a ranar Laraba a Abuja.
Ya kara da cewa, d’awar ita ce farashin jigilar man fetur daga matatun mai da ma’ajiyar man fetur zuwa tashoshin mai.