fidelitybank

Karancin man fetur ka iya janyo tashin farashin kayayyaki

Date:

Shugaban Sashen Ƙididdiga na kasa, Dr Simon Harry, ya ce, ƙarancin man fetur da ake fama da shi a wasu sassan ƙasar nan, zai iya shafar hauhawar farashi a watan Fabarairu idan ba a ɗauki mataki ba.

Da ya ke jawabi a wurin taron manema labarai a ranar Talata, Dr Harry, ya ce, ƙarancin man zai haifar da fargaba kan tattalin arziki ta yadda farashin kayan abinci za su tashi da kuma ladan ayyuka.

Ya kuma ce ko a na so ko ba a so, masu safarar kaya za su yi amfani da wannan damar wajen ƙara kuɗin dako.

Dailytyrst ta rawaito cewa, Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce, an samu raguwa a hauhawar farashin kaya a Najeriya a watan Janairun da ya gabata da kashi 0.34 cikin 100 idan aka kwatanta da Disamban 2021.

Yanzu haka dai ana sayar da lita ɗaya ta man fetur ɗin kan kai Naira 500 ko fiye a Abuja, yayin da gidajen mai ƙalilan ne ke sayar da man.

A gefe guda kuma, kamfanin mai na Najeriya, NNPC, ya ce, ya bayar da umarnin dakon mai daga manyan rumbuna da kuma sayar da shi a gidajen mai a fadin kasar, ba dare ba rana a kokarin kawo karshen matsalar.

A wata sanarwa da kamfanin ya fitar jiya Talata, NNPC ya ce yana ba wa ‘yan kasar tabbacin daukar matakan da suka dace domin hanzarta samar da man a fadin kasar.

www.punch news.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp