fidelitybank

Karancin kudi zai kawo cikas wajen kidayar ‘yan Najeriya – Agba

Date:

Ƙaramin ministan kasafin kuɗi da tsare-tsare Clem Agba, ya bayyana damuwa kan tasirin da rashin isassun kuɗi da matsalar tsaro da kuma bambance-bambancen al’adu za su yi wa aikin ƙidayar jama’a da za a yi a ƙasar cikin wannan shakara.

An dai tsara gudanar da ƙidayar ne tsakanin ranakun 29 ga watan Maris zuwa biyu ga watan Afrilun wannan shekara.

Mista Agba ya bayyana hakan ne ranar Litinin a wata ganawa da ya yi da ƙungiyoyi masu zaman kansu da da sauran masu ruwa-da-tsaki a Abuja da nufin tattauna ɓangarorin da za su iya kawo tarnaƙi ga aikin ƙidayar.

Ministan ya ƙara da cewa gwamnati ta fitar da fiye da kashi 60 na kuɗaɗen da ake buƙata domin aikin, inda ya ƙara da cewa yanzu ana jiran masu ruwa-da-tsaki da ƙungiyoyi masu zaman kansu da su bayar da nasu kason.

Ganawar dai ita ce ta biyu da jami’an hukumar ƙidaya ta ƙasar ke yi da ƙungiyoyin da za su taimaka wajen gudanar da shirin a shirye-shiryen gabatar daƙidayar jama’ar.

Ɗaya daga cikin maƙasudin ganawar shi ne yadda za a samara kudin gabatar da ƙidayar, inda hukumar ya yi alƙawarin gudanar da komai a bayyane.

Duk da cewa an samu matsalolin tsaro a lokacin aikin gwajin da aka yi a wasu ƙananna hukumomin ƙasar, shugaban hukumar ƙidayar ya kawar da fargabar da wasu ke yi na cewa ba za a yi aikin a wasu sasan ƙasar ba.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp