Kusan kwanaki takwas ya rage zaben 2023, jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP, dan takarar shugaban kasa, Rabi’u Kwankwaso ya bayyana irin ‘yan takarar da bai kamata ‘yan Najeriya su goya baya ba.
Kwankwaso ya ce, bai kamata ‘yan Najeriya su goyi bayan ‘yan takarar da ake da shakku kan takardar shaidar karatunsu ba.
Da yake jawabi a wani taro da dalibai a garin Keffi na jihar Nasarawa, Kwankwaso ya kuma yi gargadin a guji marawa ‘yan takara da sabani kan shekarun su.
Kwankwaso ya ba da shawara, “Kada ku tallafa wa mutanen da ba su da satifiket kuma waɗanda ba su san shekarun su ba.
“Kada ka goyi bayan mutanen da, idan ka tambaye su game da shekarunsu, suna jin zagi, kuma kada ka goyi bayan mutanen da suke son tilasta wa mutane irin su.
“Abin takaici ne matuka a ce muna da kasa mai rabe-rabe. Zan yi WASSCE da NECO kyauta ga duk ’yan Najeriya, kamar a baya, za mu tabbatar da tallafin karatu ga dalibai inda yaran talakawa za su iya zuwa makaranta.”