fidelitybank

Kar ku yi mamaki cewa Tinubu ya na da hannun jari a Manchester United – Jibrin

Date:

Daraktan kamfen din Bola Tinubu, Abdulmumin Jibrin, ya bayyana irin tarin dukiyar da Bola Tinubu ya ke da ita, sakamakon cece-kuce da a ke yi a kai.

A wata hira da Jibrin ya yi da gidan talabijin na Channels ya ce, Tinubu tun kafin ya shiga siyasa mai tarin arziki ne, domin ya yi aiki da kamfanin mai na Mobil da wasu manyan kamfanoni.

Ya bayyana cewa, jama’a za su yi mamaki idan ya sanar da cewa Tinubu ya na da hannun jari a kungiyar kwallon kafa ta Manchester United.

Ya ce, tushen arzikin shugaban Jam’iyyar APC ta kasa bai taba zama dalilin tada kura ba,inda yace hakan abu ne bayyananne.

Kamar yadda tsohon dan majalisar ya ce, kungiyoyin kasashen duniya sun dade suna bibiyar Tinubu, tun daga rayuwar da ya yi a makaranta, inda ya ce, tsohon gwamnan Legas din ya yi aiki a kamfanin Mobil da wasu kamfanoni kafin ya fada siyasa. Kuma Tinubu bai shigo siyasa a fakiri ba.

“Zan iya tabbatar muku da cewa, duk sanatocin Najeriya babu talaka, kuma ya shigo siyasa a matsayin sanata. Ya na da hanyoyin samun kudi, mutumin nan kasuwanci a jinin sa yake. Ya na kasuwanci tsakanin kasa da kasa. Duk mutanen da ke cece-kuce game da shi sun sani sarai cewa, ya na daukan nauyin hidindimun siyasar sa, ba tare da wani ya tallafa ma sa ba, tun a tsakiyar karni na 19”. In ji Jibrin.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp