Jam’iyyar New Nigerian Peoples Party (NNPP) ta bukaci ‘yan Najeriya da kada su karaya kan cece-kucen da ake yi na nuna sha’awar tsayawa takarar shugaban kasa, da gwamnan babban bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefele ya yi.
Shugaban NNPP na kasa, Farfesa Rufa’i Alkali, a wata ganawa da manema labarai a sakatariyar jam’iyyar a Abuja, ya ce duk da cewa zarge-zargen siyasar Emefele a lokacin da yake kan karagar mulki ta jefa wani duhu a cikin harkokin zaben kasar, “duk da haka, sahihancin zaben ya dogara ga ‘yan Najeriya.”
An yi ta cece-ku-ce a tsakanin al’umma biyo bayan doguwar sha’awar da Gwamnan CBN ya yi na tsayawa takarar Shugaban kasa a zaben 2023.