fidelitybank

Kar ku bata wa Yarinya rayuwa a kan sakamakon JAMB – Keyamo

Date:

Tsohon Ministan Kwadago da Aiki, Festus Keyamo, ya mayar da martani kan sakamakon kwamitin da Gwamnan Jihar Anambra, Charles Soludo ya kafa, domin ya binciki cece-kucen da ke tsakanin Hukumar Shirya Jarrabawar Shiga Jami’o’i ta JAMB da Ejikeme Mmesoma kan sakamakonta na UTME.

Keyamo ya bayyana Mmesoma a matsayin hazikin yarinya, inda ya shawarci al’ummar kasar su yi taka tsantsan kada su halaka ta, inda ya ce abin da take bukata shi ne nasiha, gyara da kuma jagora.

Bincike ya nuna Mmesoma ta ƙirƙiri maki 362 da ta ke nunawa sabanin ingantacciyar maki, 249.

A wata sanarwa da ya fitar ta shafin Twitter da aka tabbatar a ranar Asabar, tsohon Ministan, wanda ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici, ya ce da gangan ya jira karshen binciken kafin ya yi tsokaci kan labarin.

Keyamo ya kuma shawarci iyayenta da su kara mata kwarin guiwa da ta yiwa hukumar JAMB da iyalanta da ‘yan Najeriya hakuri, sannan a bar ta ta samu gurbin karatu a bisa hakikanin maki.

Ya rubuta cewa, “Na jira karshen wannan bincike da gangan kafin in yi tsokaci kan wannan mummunan lamari na ‘yarmu Mmesoma Ejikeme.

“Yarinya ce haziki, idan aka yi la’akari da ainihin maki 249. Ya kamata al’umma su yi hattara kar su halaka ta. Abin da take bukata shi ne nasiha, gyara da kuma jagora. Babu shakka ba ta san nauyi da nauyin abin da take yi ba. A matsayinmu na matasa, yawancinmu mun yi kurakuran yara waɗanda ba su taɓa fitowa fili ba.

“Ya kamata iyaye su karfafa mata ta yi hakuri da jama’a ga hukumar JAMB, ga iyalanta da kuma ‘yan Najeriya daga nan sai a ba ta damar samun gurbin karatu a bisa hakikanin maki. Duk wanda har yanzu yana tura wasu ruwayoyi akan wannan batu ba ya taimaka mata da danginta.

“Lokaci ya yi da za a rufe wannan babin mara dadi kuma mu ci gaba. Wannan ita ce rokona.”

legitnews.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp