fidelitybank

Kar ku bari a yi amfani daku a matsayin bangar siyasa – CAN

Date:

Gamayyar kungiyoyin matasan Kirista a karkashin kungiyar Christian Association of Nigeria Youth Wing, a Abuja, a ranar Lahadi, sun shawarci ‘yan Najeriya da kada su bari a yi amfani da su a matsayin ‘yan bangar siyasa a zaben 2023.

Matasan kiristocin sun bukaci ‘yan Najeriya da su kare kuri’unsu da tabbatar da hakan ya yi daidai da muradin ‘yan kasar.

Belusochukwu Enwere, shugaban kungiyar YOWICAN ta kasa a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya kuma gargadi jama’a game da tashe-tashen hankulan zabe amma ya bukaci jama’a da su kare kansu daga masu kashe mutane a duk wata riga da za ta kawo cikas ga gudanar da zaben na badi.

Ya ce, “Kungiyar, a matsayinta na babbar mai ruwa da tsaki a harkokin zabe, za ta fara yakin neman zaman lafiya a duniya, na yaki da tashe-tashen hankula a duk sassan kasar.”

Ya kuma bukaci ‘yan Najeriya da su dauki kahon bijimin ta hanyar rungumar zaman lafiya ko ta halin kaka da kuma kowane mataki na babban zaben shekara mai zuwa.

Enwere, ya koka da yadda zaben 2023 ke kara karatowa, kuma al’ummar kasar na fama da matsalolin rashin tsaro daban-daban kamar su garkuwa da mutane, ‘yan fashi, makiyaya, ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba, da dai sauran kalubale.

Shugaban kungiyar YOWICAN ya bayyana cewa dole ne ‘yan Najeriya su gargadi jam’iyyun siyasa da su bi ka’idojin wannan wasa.

www.legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...
X whatsapp