fidelitybank

Kar CBN ya dage wa’adin da ya bayar saboda masu magudin zabe – Atiku

Date:

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya yi kira ga babban bankin Najeriya, CBN, da kada ya dage wa’adin karbar tsofaffin naira, bayan 10 ga watan Fabrairu.

An bayyana hakan ne a wata sanarwa da kungiyar yakin neman zaben Atiku ta fitar a ranar Laraba.

Atiku ya ce masu yin magudin zabe na da burin tura CBN ya tsawaita wa’adin zuwa ranar 25 ga watan Fabrairu da 11 ga Maris domin cimma burinsu.

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya bukaci babban bankin kasar da ya gaggauta binciki matakan da ya sanya a gaba domin tabbatar da zagayowar sabbin takardun kudi na Naira tare da saukaka wahalhalun da ‘yan Najeriya ke fuskanta a halin yanzu musamman mazauna karkara.

Karanta Wannan: Obi da Kwankwaso ba barazana ce a gareni ba – Atiku

Wani bangare na sanarwar ya kara da cewa: “Bai kamata a sake dage tsarin mulkin na Naira ba bayan karewar wa’adin ranar 10 ga watan Fabrairu.

“Masu magudin zabe suna neman tura CBN ya tsawaita har sai bayan zabe da sun cimma munanan makircinsu.

“Ya kamata CBN da Fadar Shugaban Kasa su tsaya tsayin daka. Amfanin sabuwar manufar Naira ya zarce kadan daga cikin matsalolin da muke fuskanta.”

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...
X whatsapp