fidelitybank

Kar a sake a miƙa Hamdiyya hannun Ƴansanda – Amnesty

Date:

Ƙungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International a Najeriya ta soki matakin da hukumomi ke shirin ɗauka na miƙa matashiyar nan da aka gano a jihar Zamfara, Hamdiyya Sharif ga jami’an ƴansanda.

Shugaban ƙungiyar Mallam Isa Sanusi ya shaida wa BBC cewa bayanan da suke samu shi ne kwamishinan ƴansanda jihar Zamfara ya nace sai an mayar da Hamdiyya Sharif ga hukumar ƴansandan Sokoto, maimakon ba ta kulawar likitoci, wanda a cewarsa shi ta fi buƙata a halin yanzu.

”Mu yanzu abin da muka fahimta a taƙaice shi ne kenan an kamata, ko kuma sun riƙe ta”, in ji shi.

Mallam Isa Sanusi ya yi kira ga hukumomin Najeriya su bai wa matashiyar kariya saboda yadda rayuwarta ke cikin ”barazana”.

A yammacin ranar Laraba ne aka gano Hamdiyya Sherif a wani ƙauye cikin jihar Zamfara, bayan ɓatan-dabo da ta yi a ranar Talata a jihar Sokoto.

A bayanan da wata makusanciyar Hamdiyya ta yi wa BBC, ta ce wasu mutane ne suka sace matashiyar tare da yi mata wata allura, lamarin da ya kai ga fita daga cikin hayyacinta, inda daga baya ta tsinci kanta cikin wani daji a jihar Zamfara mai maƙwaftaka.

Sanarwar Amnesty ta ce “yanzu haka rayuwar Hamdiyya Sharif na cikin haɗari, kuma wajibi ne hukumomin Najeriya su ba ta kariya”.

Hamdiyya na fuskantar shari’a a kotu, inda gwamnatin jihar Sokoto, da ke arewa maso yammacin Najeriya ke tuhumar ta da zargin yunƙurin tayar da zaune tsaye bayan ta yi wani bidiyo tana sukar gwamnati kan rashin ɗaukan matakan da suka dace kan matsalar tsaro.

Sokoto na cikin jihohin Najeriya da ke fama da matsalar ƴan fashin daji masu kisa da kuma garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.

Ƙauyuka da dama sun yi ƙaura sanadiyyar kashe-kashen wanda ya ƙi ci ya ƙi cinyewa duk da ƙoƙarin da gwamnati ta ce tana yi wajen yaki da matsalar.

Amnesty International da lauyoyin Hamdiyya na nuna yatsa ga gwamnatin jihar Sokoto, wadda suka ce tana ƙoƙarin rufe bakin masu suka, lamarin da suka ce ya saɓa tsarin ƴancin fadin albarkacin baki.

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...
X whatsapp