fidelitybank

Kar a sake a miƙa Hamdiyya hannun Ƴansanda – Amnesty

Date:

Ƙungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International a Najeriya ta soki matakin da hukumomi ke shirin ɗauka na miƙa matashiyar nan da aka gano a jihar Zamfara, Hamdiyya Sharif ga jami’an ƴansanda.

Shugaban ƙungiyar Mallam Isa Sanusi ya shaida wa BBC cewa bayanan da suke samu shi ne kwamishinan ƴansanda jihar Zamfara ya nace sai an mayar da Hamdiyya Sharif ga hukumar ƴansandan Sokoto, maimakon ba ta kulawar likitoci, wanda a cewarsa shi ta fi buƙata a halin yanzu.

”Mu yanzu abin da muka fahimta a taƙaice shi ne kenan an kamata, ko kuma sun riƙe ta”, in ji shi.

Mallam Isa Sanusi ya yi kira ga hukumomin Najeriya su bai wa matashiyar kariya saboda yadda rayuwarta ke cikin ”barazana”.

A yammacin ranar Laraba ne aka gano Hamdiyya Sherif a wani ƙauye cikin jihar Zamfara, bayan ɓatan-dabo da ta yi a ranar Talata a jihar Sokoto.

A bayanan da wata makusanciyar Hamdiyya ta yi wa BBC, ta ce wasu mutane ne suka sace matashiyar tare da yi mata wata allura, lamarin da ya kai ga fita daga cikin hayyacinta, inda daga baya ta tsinci kanta cikin wani daji a jihar Zamfara mai maƙwaftaka.

Sanarwar Amnesty ta ce “yanzu haka rayuwar Hamdiyya Sharif na cikin haɗari, kuma wajibi ne hukumomin Najeriya su ba ta kariya”.

Hamdiyya na fuskantar shari’a a kotu, inda gwamnatin jihar Sokoto, da ke arewa maso yammacin Najeriya ke tuhumar ta da zargin yunƙurin tayar da zaune tsaye bayan ta yi wani bidiyo tana sukar gwamnati kan rashin ɗaukan matakan da suka dace kan matsalar tsaro.

Sokoto na cikin jihohin Najeriya da ke fama da matsalar ƴan fashin daji masu kisa da kuma garkuwa da mutane domin neman kudin fansa.

Ƙauyuka da dama sun yi ƙaura sanadiyyar kashe-kashen wanda ya ƙi ci ya ƙi cinyewa duk da ƙoƙarin da gwamnati ta ce tana yi wajen yaki da matsalar.

Amnesty International da lauyoyin Hamdiyya na nuna yatsa ga gwamnatin jihar Sokoto, wadda suka ce tana ƙoƙarin rufe bakin masu suka, lamarin da suka ce ya saɓa tsarin ƴancin fadin albarkacin baki.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp