Rundunar ‘yan sanda ta ja kunnen masu zuwa da Karnuka ko wasu nau’ikan dabbobi a rumfunan zaɓe musamman a ranar zaɓe.
A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ya fitar, ta ce sashe na 126 na dokar zaɓe ta 2022 ya bayyana ƙarara cewa yin hakan saɓa doka ne, kuma laifi ne da aka tanadar wa hukunci ƙarƙashin dokar riƙe makami domin razana masu kaɗa ƙuri’a da jami’an zaɓe.
Sanarwar ta ƙara da cewa ana ɗaukar karnuka a matsayin makamin da masu su ke amfani da su domin razanarwa ko cin zarafi ko raunata jama’a.
”Aƙidar zuwa da karnuka rumfunan kaɗa ƙuri’a da masu zaɓe, ko wasu gungun mutane ke yi ba abu ne da za a lamunta ba, kuma muna kira da a dakatar da yin hakan, saboda ya saɓa da dokar zaɓe domin kuwa hakan na janyo razani da tsoratarwa”, in ji sanarwar.
Daga ƙarshe sanarwar ta gargaɗi masu niyyar zuwa da karnuka ko sauran nau’ikan dabbobin rumfunan zaɓe da su guji yin hakan, saboda a cewar rundunar hakan saɓa dokar zaɓen ƙasar ne.