fidelitybank

Kar a je da Karnuka waje zaɓe -Ƴan Sanda

Date:

Rundunar ‘yan sanda ta ja kunnen masu zuwa da Karnuka ko wasu nau’ikan dabbobi a rumfunan zaɓe musamman a ranar zaɓe.

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ya fitar, ta ce sashe na 126 na dokar zaɓe ta 2022 ya bayyana ƙarara cewa yin hakan saɓa doka ne, kuma laifi ne da aka tanadar wa hukunci ƙarƙashin dokar riƙe makami domin razana masu kaɗa ƙuri’a da jami’an zaɓe.

Sanarwar ta ƙara da cewa ana ɗaukar karnuka a matsayin makamin da masu su ke amfani da su domin razanarwa ko cin zarafi ko raunata jama’a.

”Aƙidar zuwa da karnuka rumfunan kaɗa ƙuri’a da masu zaɓe, ko wasu gungun mutane ke yi ba abu ne da za a lamunta ba, kuma muna kira da a dakatar da yin hakan, saboda ya saɓa da dokar zaɓe domin kuwa hakan na janyo razani da tsoratarwa”, in ji sanarwar.

Daga ƙarshe sanarwar ta gargaɗi masu niyyar zuwa da karnuka ko sauran nau’ikan dabbobin rumfunan zaɓe da su guji yin hakan, saboda a cewar rundunar hakan saɓa dokar zaɓen ƙasar ne.

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp