fidelitybank

Kante ya bi sahun Benzema zuwa Al-Ittahad

Date:

N’Golo Kante ya saka hannu kan yarjejeniyar kaka uku da Al-Ittihad ta Saudiyya, kamar yadda wata majiya ta sanar wa kamfanin dillacin labarai na AFP.

Dan kwallon tawagar Faransa ya je kungiyar kwana daya bayan tsohon dan wasan Real Madrid, Karim Benzema ya koma Al-Ittihad.

Kante, mai shekara 32, ya je an auna koshin lafiyarsa daga baya ya saka hannu kan kunshin yarjejeniya, kamar yadda majiyar ta sanar da labarin cewar ba a ba ta izinin bayyana batun daukar Kante ba.

Kante wanda ya bar Chelsea a kakar nan, ya lashe kofin duniya a 2018 a Rasha tare da tawagar Faransa, kuma a halin yanzu yana fama da raunin da ya yi jinyar wata shida.

Majiyar ba ta fayyace kan kudin da Kante ya amince da kunshin yarjejeniyar buga gasar kwallon Saudi Arabia ba.

Ranar Talata Al-Ittihad ta sanar da daukar Benzema, mai shekara 35, shima kan kwantiragin kaka uku, bayan da yarjejeniyar ta kare a bana da Real Madrid.

Benzema da Kante da kyaftin din Argentina, Lionel Messi, na cikin ‘yan kwallo 10 da Saudiyya ta tsara dauka, domin bugawa a gasar tamaula na kasar.

daily post nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin Æ´an Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taÉ“a barin Iran ta Æ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaÆ™i – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama É—an kasar China da zargin kai wa Æ´an Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp